Yadda Za’ayi Maganin Olsa (Ulcer) Komai tsananinta. Da izinin Allah

 Yadda Za’ayi Maganin Olsa (Ulcer) Komai tsananinta. Da izinin Allah 




Olsa (Ulcer) cuta ce dakan addabi Al’ummar wannan zamani da muke ciki wanda zaka samu yawanci ana ɗauke da ita, wanda wasu mutanen sun san ita ke damunsu wasu kuma basu sani ba.

Akwai alamomin da olsa (Ulcer) take dashi dayawa wanda wasu da dama basu san cewa itake damunsu ba. Don haka Zamu kawo wasu daga cikin alamomin cutar Olsa (Ulcer) kamar haka: 


Karanta Yadda Mata Zasu Gane Miji Nagari 

Ciwon Ciki,Amai mai tsami,Jiki ya Dinga Rawa Idan Kanajin Yunwa,

Rashin Son Cin abinci,Yawan yin Gyatsa,Ciwon Ƙirji,Kashin Jini,Ramewa,Kasalar Jiki,Zafin Ƙirji.

Dadai sauransu domin akwai wasu alamominta da dama

Yadda Za’a Magance ta.

Ga masu Olsar dabata zama Chronic ba wanda sukeji zafin ƙirji ko ciwon ciki.

Zasu nemi Ayaba mai kyau babba guda ɗaya idan kuma ƙarama aka samu guda biyu sai ayi blending dinta ko kuma a kirɓa ta sosai Sai a samu madarar ruwa kota gari kowacce iri saiku haɗa Ayaba da madara kamar cikin kofi guda sai a dinga sha da safe kafin aci abinci, bayan kayi kamar mintuna 30 dasha sai kuci abincin ku. Sai kuma kofi guda bayan anci abincin dare.

In Allah ya yarda wannan Ciwo zai warke da yardar Allah.

SAI KUMA MASU BABBAR OLSA (ULCER) WATO CHRONIC.

Zaku Nemi:

Habbatussauda,Garin Magarya.

Habbatussauda

Zaku nemi Habbatussauda mai kyau a kasuwa, zaku dakata sosai tazama gari, saiku kawo garin Magarya a haɗa a dinga tafasa a saka zuma a ciki a dinga sha Safe, Rana da kuma dare.

Shima wannan Indai an maida hankali da yinsa to Insha Allahu za’a rabu da ita. Da izinin Allah 

Allah yabada sa a 

Kuma Ina ganin fatan alkairin da ake yi mun kuma ina godiya Allah yabar zumunci 

Ni Fatana arayiwa itace na taimaki bayin Allah dake fama da lalura ajikinsu amma basu San magungunan da zasuyi domin rabuwa da wannan ciwoba' 

Kuma addu a ta itace Allah yasa dukkan Wanda na dau magani nabasa" ko nayi bayanin maganin ya dauka ya aikata' Allah yasa karshen wahalarsa kenan" 

Allah yasa mudace 

Malam Aminu

Post a Comment

Previous Post Next Post